Tyla ta cire Najeriya daga cikin jerin ƙasashen da za ta ziyarta a rangadin duniya da ta shirya domin tallata sabon kundin waƙoƙinta.

Da farko, an tsara cewa mawaƙiyar za ta gudanar da wasa a Legas ranar 22 ga Disamba, a matsayin ɗaya daga cikin wasanninta uku da aka tsara a nahiyar Afirka.

Sai dai, bayan sanar da jadawalin rangadin a ranar Litinin, an cire Najeriya daga cikin jerin wuraren da za ta kai ziyara.

Rahotanni sun nuna cewa matakin na zuwa ne bayan ce-ce-ku-ce da suka biyo bayan hare-haren nuna ƙyamar baƙi da suka faru a Afirka ta Kudu, lamarin da ya janyo muhawara tsakanin 'yan Najeriya da wasu 'yan Afirka ta Kudu.

Har zuwa yanzu, Tyla ko tawagarta ba su fitar da wata sanarwa a hukumance da ke bayyana dalilin cire Najeriya daga cikin jadawalin rangadin nata.