Sabuwar waƙar siyasa da fitaccen mawaƙin Hausa Dauda Kahutu Rarara ya saki ta jawo muhawara a kafafen sada zumunta bayan ta ƙunshi zarge-zarge kan tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa Ali Pantami.
A cikin waƙar, Rarara ya yi zargin cewa Pantami na amfani da miyagun ƙwayoyi, tare da bayyana goyon bayansa ga ɗan takarar gwamnan jihar Gombe na jam'iyyar APC, Dakta Jamilu Isyaku Gwamna.
Pantami kuwa ana bayyana shi a matsayin ɗan takarar gwamnan jihar Gombe na jam'iyyar PDP, mai samun goyon bayan Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike.
Sai dai, tun bayan fitar da waƙar, mutane da dama sun soki abin da ke cikinta, inda wasu ke cewa maimakon ta rage wa Pantami farin jini, ta ƙara jawo masa goyon baya da tausayi daga jama'a.
Dalung Ya Soki Salon Waƙoƙin Siyasa
Tsohon Ministan Wasanni da Raya Matasa, Solomon Dalung, ya nuna damuwa kan yadda waƙoƙin siyasa ke rikidewa zuwa cin mutunci da zarge-zarge marasa hujja.
A cewarsa, a da waƙoƙin siyasa a Arewacin Najeriya na ilmantarwa, wayar da kai da ƙarfafa haɗin kan al'umma, amma yanzu an mayar da su hanyar bata suna.
Dalung ya ce:
"Idan Sheikh Pantami ya yi kuskure, a kalubalanci abin da hujjoji. Idan siyasar sa ta saba wa juna, a bayyana hakan. Amma cin mutunci da zarge-zarge marasa hujja ba su dace da al'adunmu ba."
Ya kuma yi kira da a kiyaye dabi'un Arewa na mutunci, kunya da girmama juna duk da bambancin siyasa.
Masu Sharhi Sun Yi Martani
Wani mai sharhi daga jihar Adamawa, Abdulaziz Jauro, ya ce amfani da salon waƙa ko karin magana ba ya mayar da zargin bata suna zuwa fasaha.
Shi ma lauya kuma mai fafutukar kare haƙƙin ɗan Adam, Nuhu Dantani, ya bayyana cewa waƙar na iya yin illa ga yaƙin neman zaɓen ɗan takarar APC a Gombe.
A cewarsa, duk da kasancewarsa mai goyon bayan Dakta Jamilu Isyaku Gwamna, yana ganin waƙar ta ƙara wa Pantami farin jini da karɓuwa a idon jama'a.
Har Yanzu Ba A Ji Ta Bakin Pantami Ba
Ya zuwa yanzu, Farfesa Isa Ali Pantami bai fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan zarge-zargen da ke cikin waƙar, haka kuma babu wata hujja da aka gabatar a fili da ke tabbatar da zargin amfani da miyagun ƙwayoyi da aka yi masa.
Lamarin na ci gaba da haifar da muhawara kan iyakar da ya kamata waƙoƙin siyasa su tsaya a kai, musamman game da amfani da zarge-zarge marasa hujja da cin mutunci a yaƙin neman zaɓe.