Legas – Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa babban kuskuren da ya taɓa aikatawa a rayuwarsa ta siyasa shi ne zaɓen Atiku Abubakar a matsayin mataimakin shugaban ƙasa a shekarar 1999.
Obasanjo ya bayyana hakan ne a ranar Juma'a yayin ƙaddamar da Charly Boy Foundation da kuma littafin tarihin rayuwar Charles Oputa (Charly Boy), 999: A Memoir in Tribute to Late Justice Chukwudifu Oputa, da aka gudanar a Legas.
Da yake amsa tambaya kan muhimman shawarwarin da ya yanke a lokacin mulkinsa, tsohon shugaban ƙasar ya ce da ace ya san Atiku kamar yadda ya san shi daga baya, da bai zaɓe shi a matsayin mataimakin shugaban ƙasa ba.
"Mutumin da na zaɓa ya zama mataimakina. Da ace na san shi kamar yadda na san shi daga baya, da ban zaɓe shi ba," in ji Obasanjo.
Lokacin da aka tambaye shi ko Atiku yake nufi, Obasanjo ya tabbatar da cewa tsohon mataimakin shugaban ƙasar yake magana a kansa.
Sai dai ya jaddada cewa duk da ra'ayinsa, ba ya riƙe da wata ƙiyayya ta kashin kai ga Atiku.
Yadda Dangantakarsu Ta Lalace
Obasanjo da Atiku sun yi aiki tare daga shekarar 1999 zuwa 2007, amma daga baya dangantakarsu ta lalace sakamakon sabanin siyasa, musamman kan batun yunƙurin yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulki domin bai wa Obasanjo damar yin wa'adi na uku.
Rikicin ya ƙara tsananta ne kafin zaɓen 2007, lokacin da Atiku ya bar jam'iyyar PDP zuwa Action Congress (AC) domin tsayawa takarar shugaban ƙasa.
A lokacin rikicin, gwamnatin Obasanjo ta yi yunƙurin ayyana kujerar mataimakin shugaban ƙasa a matsayin wacce babu mai riƙe da ita, amma Kotun Ƙoli ta yanke hukuncin cewa shugaban ƙasa ba shi da ikon tsige mataimakin shugaban ƙasa da aka zaɓa ta hanyar zaɓe.
Siyasar 2027
Sabbin kalaman Obasanjo na zuwa ne yayin da siyasar zaɓen shekarar 2027 ke ƙara ɗaukar hankali.
Atiku Abubakar, wanda ake bayyana a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC, ya taɓa zargin Obasanjo da nuna goyon baya ga wani ɗan takara ba tare da bayyana hakan a fili ba.
Haka kuma, Atiku ya musanta zarge-zargen da ake sake tayarwa cewa ya bai wa marigayi tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Na'Abba, kuɗi domin ya jagoranci yunƙurin tsige Obasanjo daga mulki, yana mai cewa zargin na da manufar ɓata masa suna kafin zaɓen 2027.
Ya zuwa yanzu, Atiku Abubakar bai fitar da wata sabuwar sanarwa kai tsaye ba domin mayar da martani kan kalaman da Obasanjo ya yi a taron da aka gudanar a Legas.