Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, ya gargadi al'umma kan tsallaka danja kafin ba da hannu, tare da jaddada muhimmancin bin dokokin zirga-zirga.
Daraktan Yaɗa Labaran Gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da ya fitar a yau talata.
Sanarwar ta bayyana cewa gwamnan ya yi wannan gargaɗi ne yayin da ya shafe sama da awa ɗaya a mahadar Kofar Fanfo yana sa ido kan yadda masu ababen hawa kan bin danja.
Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnan ya buƙaci direbobi, masu Adaidaita Sahu da masu tafiya a ƙafa su bi dokokin zirga-zirga domin kare rayuka da dukiyoyi.
Haka kuma ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta sake fasalin Hukumar KAROTA domin ƙarfafa kula da zirga-zirga da tabbatar da bin dokokin hanya a faɗin jihar.