Gwamnatin Najeriya da ta Isra'ila sun sake jaddada aniyarsu ta ƙara ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu a fannonin tsaro, tsaron ƙasa, noma, fasaha, lafiya da kasuwanci.

An bayyana hakan ne yayin ziyarar ban girma ta bankwana da jakadan Isra'ila mai barin gado a Najeriya, Michael Freeman, ya kai wa Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, a Abuja.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka wa ministar kan harkokin yaɗa labarai, Magnus Eze, ya fitar, Bianca Odumegwu-Ojukwu ta yaba wa jakadan bisa nasarar da ya samu a lokacin aikinsa, tana mai cewa ya shimfiɗa ingantacciyar hanya ga wanda zai gaje shi.

Ta kuma sake jaddada ƙudirin Gwamnatin Tarayya na zurfafa haɗin gwiwa da Isra'ila a fannonin yaƙi da ta'addanci, tattara bayanan sirri da kuma gina ƙwarewar jami'an tsaro. Haka kuma, ta ce Najeriya na son cin gajiyar ƙwarewar Isra'ila wajen tsaron iyakoki da gudanar da harkokin ruwa.

A nasa ɓangaren, Jakada Michael Freeman ya tabbatar da cewa Isra'ila za ta ci gaba da faɗaɗa haɗin gwiwa da Najeriya. Ya bayyana cewa yawan cinikayyar da ake yi tsakanin ƙasashen biyu, wanda ya kai kusan dala miliyan 200 a shekara, har yanzu bai kai matakin da ake sa ran zai kai ba.

Freeman ya bayyana Najeriya a matsayin ƙasa mai dimbin damammaki, tare da alƙawarin ci gaba da aiki domin bunƙasa alaƙar da ke tsakanin ƙasashen biyu da kuma cimma cikakken moriyarta.